Uncategorized

Bani da niyyar komawa gidan tsohon mijina Sani Danja, cewar Mansurah Isah

Bani da niyyar komawa gidan tsohon mijina Sani Danja, cewar Mansurah Isah

Tsohuwar fitacciyar jaruma a masana’atar Kannywood wadda ta taka rawar gani, tsohuwar matar fitaccen jarumi kuma mawaki a masana’atar Kannywood Mansurah Isah tace sam bata da niyar koma gidan tsohon zumanta.

Ana fira da ita a gidan tarin Dw inda mai gabatarwa yake mata tambaya.

Me kike kewa da sani danja?

Tayi dariya ta nuna cewa mai gabatarwa yana neman magana a wajen ta ne amma a cikin raha.

Ina komawa gidan sani danja ?

“A gaskiya kana tambaya ta da sani danja ance zo mu zauna zo mu saɓane , amma gaskiya bana kewar komai saboda dai-dai ne bazan iya ja da ikon Allah ba. A gaskiya bana shirin kome kuma baya cikin tsarina ba yanzu ba, kuma ba nan gaba ba, amma kuma mutum bai san rufi sa ba”- ji mansurah isah.

Ina tabbatar cewa ƴan fim ba su zaman aure?.

A toh ban san inda sunka samu yan fim basa aure ba, saboda a cikin al’umma da ake biliyoyi mu da ko dubu bamu wuce ba ina anka bar sauran , wannan son kai ne da son rai da son zuciya a cikin al’umma.

Ga bidiyon shirar a kasa domin ku kalla.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button